Harbi a Villa: An Saki Hadiman Aisha Buhari

104

Sufeto Janar na ‘Yansanda, Mohammed Adamu, ya bayar da umarnin sakin ‘yansanda masu tsaron lafiyar uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, kwanaki 4 bayan an rufe su bisa harbin bindiga a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Lamarin ya haifar da kokwanton cewa ko rayuwar shugaban kasa Muhammadu Buhari na cikin hadari.

Amma fadar shugaban kasa a cikin wata sanarwa ta tabbatar da cewa Shugaba Buhari baya cikin wani hadari a kowane lokaci.

‘Yansandan sun hada da ADC na Aisha Buhari, CSP Usman Shugaba; da kwamandan rakiyarta, DSP Sheriff Kazeem da yansandan kwantar da tarzoma 4, an tsare su ranar Juma’ar da ta gabata.

An umarce su da su koma a yau domin cigaba da bincike.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

2 × five =