Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yaba wa zakaran damben Boksin na duniya ajin masu nauyi, Anthony Joshua, bisa nasarar da ya samu kan Andy Ruiz dan kasar Mexico a daren jiya Asabar.
Mahaifiyar Anthony Joshua, Yeta da kuma mahaifinsa Robert Joshua ‘yan asalin Najeriya ne duk da cewa an haife shi ne a Watford ta kasar Ingila.
Shugaban Kasar cikin sakon taya murna wanda kakakinsa, Mista Femi Adesina ya fitar a Abuja, ya taya Anthony Joshua murna inda ya jinjina masa bisa farincikin da ya saka miliyoyin ‘yan Najeriya a ciki da wajen kasarnan.
Anthony Joshua ya karbo kambunsa wanda Ruiz ya kwace daga hannunsa watanni 6 da suka gabata a Birnin New York na Kasar Amurka.
An gudanar da damben ne a Filin Wasa na Diriyah Arena a birnin Riyad na Saudiyya a gaban ‘yan kallo sama da 14,000.