Yanzu-Yanzu: Kasar Afrika ta kudu ta rufe ofishoshin jakadancinta a Nijeriya

42

Kasar Afrika ta Kudu ta rufe ofishoshin jakadancinta da ke Nijeriya sakamakon hare-haren ramuwar gayya da ‘yan Nijeriya ke kaiwa ‘yan kasar Afrika ta Kudun, kamar yadda mukaddashin jakadan kasar a nan Nijeriya Bobby Moroe ya bayyana da safiyar yau.

Moroe yace hare-haren da ake kaiwa ‘yan kasar sa  sune suka tilasta rufe ofishoshnsu har sai kura ta lafa.

Na bada umurnin rufe ofishoshin jakandancinmu har sai kura ta lafa. Mun samu labarin yadda ake kaiwa yan Afrika ta Kudu hari”

A baya dai, SkyDaily Hausa ta bada rahoton yadda aka rika kai hare-hare a kamfanoni mallakar kasar Afrika ta Kudu a Nijeriya, da kuma dawo da jakandan Nijeriya a kasar Afrika ta Kudu ya shugaba Muhammadu Buhari yayi a wani mataki na nuna bacin ran gwamnatin Nijeriya kan yadda aka kasha ‘yan kasarta a rikin kyamar baki da ya farau a wannan satin acan kasar ta Afrika ta Kudu

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

eight + 9 =