
Ministan tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi, mai ritaya, ya bukaci yan kasarnan da su fara samun kwarin gwiwar tunkarar ‘yan bindigar dake tayar da zaune tsaye a kasarnan.
Da yake zantawa da manema labarai a jiya a wajen tantance manyan hafsoshin soja da majalisar wakilai ta yi, Bashir Magashi ya bayyana wadanda suka sace dalibai da malaman makarantar sakandiren Kagara a karamar hukumar Rafi ta jihar Neja da cewa matsorata ne.
Yace hakkin yan Najeriya ne su tabbatar da cewa an samu isasshen tsaro a kewaye da su.
Ministan ya kuma yi watsi da rokon da ake yi na a kyale yan kasarnan suke daukar makamai domin kare kawunansu.
Jawabin nasa ya harzuka yan Najeriya musamman a shafukan sada zumunta, inda mutane ke zarginsa da yunkurin mayar da nauyin dake kan masu mulki zuwa kan wadanda ake mulka.