Kungiyar Lauyoyi ta kai Buhari kara bisa tsawaita wa’adin Sufeto Janar

174

Kungiyar Lauyoyi ta Kasa ta maka Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a kotu bisa karin wa’adin aikin da ya yiwa Sufeto Janar na ’Yan sanda, Mohammed Adamu.

Kungiyar ta fara daukar matakin shari’a a Babban Kotun Tarayya dake Lagos.

Wadanda ake karar a karar sun hada da shugaban kasa, da sufeto janar na yansanda da kuma hukumar kula da ayyukan yansanda.

A cikin karar, kungiyar na neman hukuncin shari’a kan yadda shugaban kasa ya tsawaita wa’adin Mohammed Adamu a matsayin Sufeto Janar na ‘yansanda na tsawon watanni uku duk da kasancewar shugaban yansandan a ranar 1 ga Fabrairun da muke ciki ya cika shekaru 35 yana aiki a matsayin dansanda.

A wata sanarwa da ya fitar a yau, shugaban kungiyar lauyoyin, Olumide Akpata, ya ce karin wa’adin ya sabawa kundin tsarin mulki, kuma kungiyar lauyoyin za ta kalubalanci rashin bin doka ko ta halin kaka.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

twenty + nine =