MAJALISAR WAKILAI TA YI ALLAH WADAI DA SACE MUTANE A JIHAR BORNO DA WASU DALIBAI A JIHOHIN KADUNA DA SOKOTO

14

Kakakin majalisar wakilai Tajuddeen Abbas,ya yi Allah wadai da sace daruruwan ‘Yan gudun hijira a Jihar Borno da wasu dalibai a Jihohin Kaduna da Sokoto.

Yayi kira ga hukumomin tsaro da su bi duk inda ‘Yan ta’addan da suka yi garkuwa da mutanen a Jihohin uku domin kubutar da wadanda harin ya rutsa da su.

Tajuddeen Abbas yayi wannan kira ne cikin wata sanarwa da hadimin sa a kafafan yada labarai Musa Abdullahi Krishi, dangane da sace dalibai a wata tsangaya dake Jihar Sokoto.

Ya kuma yi Allah wadai da ‘Yan gudun hijira da wasu dalibai a Jihar Kaduna.

Idan za’a iya tunawa ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai 15 a makarantar Islamiyyan Gidan Bakuso a karamar hukumar Gada a jihar Sokoto.

Kakakin majalisar ya bukaci sojoji da hukumomin tsaro su bi sahun masu garkuwa da mutanen don kubutar da wadanda aka sace.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

10 − 3 =