An tsige Firai-Minista bayan mummunar zanga-zangar corona a Tunisiya

34

Shugaban Kasar Tunisia, Kais Saied, ya kori Firayim Ministan kasar Hichem Mechichi tare da dakatar da majalisar kasar, bayan mummunar zanga-zangar da aka yi jiya a duk fadin kasar.

Fushi game da yadda gwamnati ta yiwa annobar corona rikon sakainar kashi, ya kara haifar da zaman dar-dar game da matsalar tattalin arzikin kasar da zamantakewar ta.

Shugaba Saied, wanda aka zaba a shekarar 2019, ya ba da sanarwar maye gurbin Firai-Ministan.

Magoya bayan sa sun barke da murna, amma ‘yan adawa a majalisar ba tare da bata lokaci ba sun zarge shi da yin juyin mulki. Rikici tsakanin kungiyoyin hamayya ya ci gaba a yau.

Kungiyoyin na jefar juna da duwatsu a wajen majalisar, wanda sojoji suka yi wa shinge, wadanda kuma suka hana ma’aikata shiga wasu gine-ginen gwamnati.

Kais Saied, wanda bashi da jam’iyya, ya dade yana adawa da mutumin da ya cire, Firayim Minista Hichem Mechichi.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

9 − five =