‘Yansandan Ghana Sun Harbe Wani Dan Najeriya Har Lahira

33

‘Yansanda a Ghana sun harbe wani dan Najeriya har lahira lokacin da ake biki a wani Otal.

Mutumin wanda ba a gane ko wanene ba, anyi zargin an bindige shi, lokacin da ‘yansanda ke kokarin tarwatsa mahalarta bikin.

A wani faifan bidiyon da abokin mamacin ya wallafa a shafin YouTube, yayi nuni da cewa an kuma kashe wani mutumin daban, wanda ba a ambaci sunansa ba, yayin hatsaniyar.

A faifan bidiyon, an ga wasu mutane sun dauke wata gawa zuwa asibiti.

Kazalika an ga wata mata a bidiyon, tana jimamin kisan, inda take cewa ‘yansandan Ghana suna kai farmaki kan ‘yan Najeriya a ko da yaushe.

An ga ‘yansanda suna kame mahalarta bikin, suna tafiya da su, ga dukkan alamu saboda taka dokar bawa juna tazara lokacin annobar corona.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

sixteen − three =