SHUGABAN KASAR LABERIYA YA KAFA KWAMITIN KWATO KADARORIN KASAR DA AKA SACE

6

Shugaban kasar Laberiya Joseph Boakai ya kafa kwamitin kar ta kwana na yaki da cin hanci da kwato kadarorin kasar da aka sace.

Mista Boakai ya bada umarnin a gano tare da gurfanar duk wani babban ma’aikaci dake da hannu a cin hanci ko satar dukiyar kasar a gwamnatin yanzu da wacce ta shude.

Bisa wannan umarni za’a dawo da duk wata kadarar gwamnati da aka mallaka ba bisa ka’ida ba.

Shugaban kasar yace a hukumce za’a magance matsalolin da suka dabai-baiye kasar.

Kazalika,dukkan wadanda suka sayi kadarar gwamnati ba bisa ka’ida ba zasu dawo da ita.

Dai-dain ‘yan kasar dake zaune a wata da ake zargin sun kwashe dukiyar al’umma za’a maida su gida.

Tuni aka ware kudaden tafiyar da wanna kwamitin wanda zai fara aiki nan ba da jimawa ba.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

thirteen + eighteen =