Buhari ya amince da kafa sabbin polytechnics 3

87

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da kafa sabbin kwalejojin polytechnics a wasu sassan kasarnan.

An sanar da amincewar cikin wata sanarwa da aka fitar yau a Abuja ta hannun daraktan hulda da jama’a na ma’aikatar tarayya ta Abuja, Ben Goong.

Daraktan yace za a kafa sabbin makarantun a jihoshin Kano, Abia da Delta.

A cewar Ben Goong, sabbin makarantun zasu fara harkokin koyo da koyarwa a watan Oktoban bana.

A wani batun kuma, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana kwarin gwiwar cewa bukatar Najeriya na fadada yankin ruwanta, a karkashin dokokin majalisar dinkin duniya na ruwa, yana bisa turba.

Shugaba Buhari ya sanar da haka yau a Abuja lokacin da ya karbi wani rahoto daga kwamitin shugaban kasa akan bukatar fadada yankin ruwan kasarnan.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

5 × 5 =