Mataimakin shugaban kasa Osinbajo, ya ziyarci mahaifan Haneefa

84

Da safiyar ranar Talata ne a jihar Kano aka wayi gari da ziyarar jaje da ta’aziya daga mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo.

Osinbajo yazo Kanon ne don jajantawa iyayen Haneefa Abubakar; wadda malaminta Abdulmalik Tanko yai wa kisan gilla.

Tini dai hukumomi a Kanon suka gurfanar da Abdulmalik a gaban kuliya tare da wasu karin mutum biyu da ake zargin suna da hannu a kisan nata.

Haneefa dai an dauke ta daga gida tsawon makonni tare da neman kudin fansa, kafin daga bisani masu garkuwar su kasheta ta hanyar bata guba.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

twelve − 1 =