Jigawa ce kan gaba cikin jihohi a rigakafin corona

32

Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta kasa ta ce ya zuwa jiya, sama da mutane miliyan 15 ne aka yiwa allurar rigakafin korona a karon farko.

Hukumar ta bayyana hakan ne a yau ta shafinta na Facebook.

A cewar hukumar, mutane miliyan 15 da dubu 110 da 459 na jimlar wadanda suka cancanta a yiwa rigakafin corona, an yi musu allurar a karon farko, yayin da mutane miliyan 5 da dubu 574 da 696 daga cikin wadanda suka cancanci allurar rigakafin, aka yi musu sau biyu.

Jihar Jigawa ce ke kan gaba, inda ta ke da mutane miliyan 1 da dubu 846 da 483 da aka yiwa rigakafin, sai jihar Legas mai mutane miliyan 1 da dubu 460 da 808 sai Kano mai mutane miliyan 1 da dubu 136 da 858.

Hukumar ta ce adadin mutanen da aka yiwa allurar rigakafin sau daya a Najeriya ya kai kashi 13.5 bisa dari na mutanen da suka cancanci rigakafin, yayin da adadin wadanda aka yi musu allurar sau biyu ya kai kashi biyar cikin 100.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

five × 3 =