Sudan ta ayyana dokar ta baci bayan an kashe mutane 50 a Darfur

93

Kasar Sudan ta ayyana dokar ta baci a jihar Dafur ta Yamma biyo bayan rikicin kabilanci da ya jawo mutuwar akalla mutane 50 da jikkata wasu 150, tare da raba dubban mutane da gidajensu.

A jiya, majalisar dinkin duniya tace akalla mutane 40 aka kashe da jikkata wasu sama da 50 bayan fada ya barke a ranar Asabar tsakanin kungiyoyin Larabawa da na wadanda ba Larabawa ba, yan kabilar Massalit da ke birnin El Geneina.

A cewar hukumar agaji ta majalisar dinkin duniya, anyi ta jin karar harbe-harben bindiga a jiya da yamma a Al Jamarik da Hay Al Jabal.

Majalisar dinkin duniya ta ce sama da mutane dubu 700 ne a yanzu tabarbarewar tsaro ya shafa a yankin, wanda yawanci hukumomi ke amfani da shi a matsayin cibiyar bayar da agaji a lardin.

A watan Janairu, rikici tsakanin yan kabilar da Massalit da Larabawa ya jawo mutuwar akalla mutane 129 da raba sama da mutane dubu 108 da gidajensu.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

4 × 1 =