MDD na neman agaji ga mutane miliyan 29 dake fama da yunwa a Sahel

27

Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin agaji biyu na kasa da kasa sun yi kira da a aike da agajin gaggawa zuwa yankin Sahel na Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Sun ce mutane miliyan 29 da ke yankunan na bukatar taimako, ciki har da yara miliyan 1 da dubu 600 da ke fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki.

Hare-haren daga masu ikirarin jihadi ya haifar da abin da Majalisar Dinkin Duniya ta kira rashin tsaro mara misaltuwa tare da raba mutane miliyan 5 da rabi da muhallansu.

Farashin abinci ya yi tashin gwauron zabi kuma yawaitar yunwa ya haura zuwa matakin mafi girma a cikin kimanin shekaru goma.

Kasashe shida da abin ya shafa sune Mali da Nijar da Burkina Faso da Chadi da wasu sassan Najeriya da Kamaru.

A wani labarin kuma, fursunoni sama da 30 sun tsere bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan motar ‘yansanda da ke jigilarsu zuwa kotun shari’a a kasar Afirka ta Kudu.

Kakakin ‘yansanda na KwaZulu Natal, Brigadier Jay Naicker, ya ce ‘yansanda na neman wadanda suka tsere.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

two × three =