Somalia ta samu jinkiri wajen gudanar da zaben shugaban kasa

67

Kasar Somaliya ta samu jinkiri wajen gudanar da zaben shugaban kasa a ranar karshe ta yau mai muhimmanci, lamarin da ya jefa kasar cikin rashin tabbas na siyasa.

Wa’adin farko na shugaban kasa mai ci Mohamed Abdullahi Farmajo Mohamed zai kare a yau.

Tattaunawa tsakanin gwamnatin tarayya da jihohin yankin kan yadda za a ci gaba da zabe ta rushe a ranar 5 ga Fabrairu.

A wata sanarwa da suka fitar a yau, ‘yan takarar shugabancin kasar na bangaren adawa sun ce za su daina amincewa da Farmajo a matsayin shugaban kasa saboda wa’adinsa ya kare.

Sun yi kira da a kafa wata kungiyar rikon kwarya wacce ta kunshi shugabannin majalisun biyu da shugabannin gwamnatocin yankuna da wakilai daga kawancensu don jan ragamar kasar zuwa ga zabe.

Sun kuma bukaci sojojin kasar ta Somaliya da su daina karbar umarni daga Shugaba Farmajo daga yau.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

nine − 5 =