Gwamnati ta haramta taruwar jama’a gabannin zanga-zanga kan zabe a Somalia

56

Gwamnatin Somaliya ta dakatar da taruwar jama’a bisa hujjar karuwar masu kamuwa da Corona.

Akwai yiwuwar matakin zai shafi zanga-zangar da aka shirya yi a gobe ta adawa da rashin tabbas a siyasar kasar bayan wa’adin Shugaban Kasa Abdullahi Farmanjo ya kare kafin a gudanar da zabe.

Majalisar ministoci ta zauna a jiya kuma ministan lafiya yayi jawabi dangane da halin da ake cikin kan cutar corona a kasar.

Ma’aikatar lafiya ta samu adadi mafi yawa na wadanda suka harbu da cutar da wadanda ta kashe a wannan watan.

Ministocin sun bayar da umarnin cewa dukkan ma’aikatan da ba na tilas ba, suyi aiki daga gida domin rage yaduwar cutar.

Kamar yadda yazo a sabon umarnin, an kuma rage tafiye-tafiye tsakanin larduna da bulaguron da ba na dole ba.

An samu mutane dubu 5 da 500 da aka tabbatar sun kamu da cutar corona a Somalia, ciki har da mutane 172 da suka mutu.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

11 − 10 =