Gwamnonin Arewa su na goyon bayan kayyade amfani da shafukan sada zumunta

69

Yunkurin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na kayyade amfani da shafukan sada zumunta ya samu goyon baya a jiya bayan gwamnoni da sauran shugabanni daga yankin Arewacin Najeriya sun bayyana goyon bayansu ga yunkurin.

Gwamnatin Buhari ta mayar da kayyade shafukan sada zumunta a matsayin abinda tafi mayar da hankali akai, inda ta zargin shafukan na sada zumunta da yada labaran kanzon kurage, wanda tace zai iya jawo rushewar kasarnan idan ba a magance ba.

Kungiyar gwamnonin Arewa a zamansu na ranar Litinin sun bayyana goyon baya ga matakin na gwamnati, wanda suka ce, za a dauka ne da nufin magance yaduwar labaran karya a kasarnan.

Zaman ganawar da aka gudanar a gidan Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna, ya samu halartar shugabanin majalisun sarakunan jihoshin Arewa 19 da sauran manyan masu ruwa da tsaki a yankin.

Kungiyar ta bayyana goyon bayan nata a takardar bayan taro da shugaban kungiyar, Gwamna Simon Lalong na jihar Filato ya bayar.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

fifteen + eleven =