An haramtawa tsohon shugaban kasa Laurent Gbagbo tsayawa takarar zabe a Ivory Coast

72
Gbagbo

Kotun kundin tsarin mulki a Ivory Coast ta haramtawa tsohon shugaban kasar Laurent Gbagbo da tsohon Fira-Minista Guillaume Soro, tsayawa takara a zaben shugaban kasar da za ayi wata mai zuwa.

Tun a baya hukumar zabe tace zata haramta tsayawa takara ga dukkan wanda yake da tarihin aikata laifi.

Dukkan mutanen biyu suna da hukunce-hukuncen da aka yanke musu.

Tun da farko, zanga-zanga ta barke a birane da dama bisa matakin shugaban kasa Alassane Ouattara na tsayawa takara a karo na uku, abinda kundin tsarin mulkin kasar ya haramta.

Mutane 15 sun mutu a rikicin tun bayan da yace zai sake tsayawa takara a watan da ya gabata.

Ya yanke shawarar tsayawa bayan wanda ya zaba a matsayin magajinsa yayi mutuwar bazata a watan Yuli.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

two × two =