Shugaba Buhari ya Tsige Shugaban Hukumar Jarabawar NECO

58
Muhammadu Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da tsige Farfesa Charles Uwakwe a matsayin shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa, NECO.

Shugaban kasar ya kuma kori mambobi 4 na majalisar gudanarwar hukumar bisa laifuka daban-daban masu alaka da badakalar kudade.

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Charles Uwakwe tun a watan Mayun 2018 bisa zargin sama da fadi da kudade tare da cin amanar aiki. Inda aka nada Abubakar Gana a matsayin shugaban riko na hukumar.

Ana zargin Charles Uwakwe tare da wasu manyan jami’ai da laifin bayar da kwangiloli a majalisar wadanda kudinsu ya kai Naira Biliyan 25, ba bisa ka’ida ba.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

18 − thirteen =