Buhari ya nada mashawarta kan bunkasa tattalin arzikin kasa

51
Muhammadu Buhari

Shugaban  kasa Muhammadu Buhari ya nada kwamitin bashi shawara kan bukasa tattalin arzikin kasa.

A cikin wata sanarwa da mai bawa shugaban kasa shawara kan yada labarai Femi Adesina ya fitar jiya Litini yace Buhari ya nada Farfesa Doyin Salami a matsayin shugaban kwamitin.

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da Dr. Muhammad Sagagi a matsayin mataimakin shugaba, sai kuma Dr. Mohammed Adaya Salisu a matsayin sakatare.

Sai kuma mambobin kwamitin wadanda suka hada da Bismarck Rewane, Prof. Chukuma Soludo, Dr. Iyabo Masha, Dr. Shehu Yahya da kuma Prof. Ode Ojowu.

A baya dai mataimakin shugaban kasa  Prof. Yemi Osinbajo ne ya jagoranci kwamitin bunkasa tattalin arzikin kasa a matsayin shugabanta.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

three − 3 =