Jami’an tsaro sun tarwatsa masu zanga-zanga a Sudan

26

Jami’an tsaro a kasar Sudan sun harba hayaki mai sa hawaye a kokarin tarwatsa zanga-zangar neman demokradiyya a babban birnin kasar Khartoum da birnin Port Sudan.

Mutane a birane dayawa na rera wakokin kin jinin sojoji tare da kiran a rushe majalisar mulkin Sudan.

Majalisar na karkashin mulkin Janar Abdel Fatah al-Burhan wanda ya jagorancin juyin mulkin sojoji a watan Oktaban bara.

A birnin Omdurman dake makotaka da Khartoum, gomman mutane sun kafa shingen ababen hawa.

Zanga-zangar na zuwa ne kwanaki 2 bayan murabus din fira-ministan kasar na farar hula, Abdalla Hamdok.

Mutane 56 ne suka mutu a jerin zanga-zanga tun daga juyin mulkin na watan Oktoba, dayawansu jami’an tsaro ne suka harbe su.

A baya an bayar da rahoton cewa an aika da jami’an tsaron Sudan zuwa sassan babban birnin kasar, Khartoum, da sauran birane, gabannin zanga-zangar.

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

3 + two =