Babu imani cikin lamuran El-rufai – Hon. Auwal

54

Sanannen matashin dan gwagwarmayar nan Hon. Auwal Yusuf, ya shawarci al’ummar jihar Kaduna cewa idan gwamnan Kaduna Nasiru El-rufai ya basu ‘notice’ a waje to su tashi kawai.

Hon. Auwal, ya bada wannan shawara ce ga al’ummar Kaduna a shafin sa na sada zumuntan facebook, inda yace “Idan malam Nasiru el-rufai ya baku notice cewa ku tashi zai rushe waje to kuyi hakuri ku tashi ku kwashe kayan bukata dana amfanin rayuwar ku domin shi (El-rufai) fa babu imani a cikin lamuran sa ballantana tausayi.

Dan gwagwarmayar ya kara da cewa “Don Allah muma talakawa mu daina taurin kai tunda mun san wannan mutumin babu digon tausayi bare sassauci a zuciyar sa”

”Kwanaki nawa ma suka rage masifar da aka jawo mana da sunan jihadi ta zama tarihi” Inji Hon. Auwal Yusuf. 

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

fourteen − seven =